Isa ga babban shafi

Human Right Watch ta zargi Facebook da sakonnin cin zarafin jama'a

Kungiyar kare hakkin bil’adama ta Human Right Watch ta zargi Facebook da dandalinsa na Instagram da cire sakonnin cin zarafin Falasdinawa yayin tashin hankali tsakaninsu da Isra'ila a wannan shekara.

dandalin sadarwa na Facebook,Instagram da WatsApp
dandalin sadarwa na Facebook,Instagram da WatsApp AP - Richard Drew
Talla

Zargin ya kara matsin lamba ga katafaren kamfanin  sadarwar ta duniya bayan da wani mai fallasa bayanan sirri ya bayyanawa 'yan majalisar dokokin Amurka a ranar Talata cewa akwai bukatar a daidaita tsarin kamfanin.

Dandalin Facebook
Dandalin Facebook Chris Delmas AFP/Archivos

Falasdinawa sun koka a bainar jama'a game da zargin yin kutse a shafukan sada zumunta a watan Mayu, yayin tashin hankali a birnin Kudus wanda ya rikide zuwa mummunan artabu na soji tsakanin kungiyoyin masu kishin Islama dake harba rokoki daga yankunan Falasdinawa, da Isra'ila wacce ta kaddamar da hare -hare ta sama.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.