Isa ga babban shafi
Saudiya

Saudiya ta jingine huldar zirga-zirga na jirage da kasashe uku

Ma'aikatar cikin gidan Saudiya ta bayyana dakatar da duk wata zirga-zirga ta jiragen sama tsakanin kasar da wasu kasashe uku da suka hada da Daular Larabawa, Habasha da kuma Vietnam.

A garin Mina, wasu daga cikin Mahajata da lamarin dakatar da zirga-zirgar jiragen sama zai shafa
A garin Mina, wasu daga cikin Mahajata da lamarin dakatar da zirga-zirgar jiragen sama zai shafa Saudi Press Agency/Handout via REUTERS
Talla

Cikin sanarwar da ta fitar, gwamnatin Saudiyan ta ce matakin da ya shafi kasashen 3 ya soma aiki ne daga yau Lahadi.

Saudiya ta ce matakin zai taimaka wajen takaita yaduwar cutar Covid-19 a cikin kasar.

A hukumance Saudiya ta gano mutane dubu 490 da suka harbu da annobar Korona, daga cikinsu kuma dubu 7 da 850 suka mutu.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.